Jeremiah 46:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ بَادَسُو أَ حَنُّنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ نٜىٰمَنْ رَنْسُ، وَتُواْ أَ حَنُّنْ سَرْكِے نٜىٰبُكَدْنٜىٰزَّرْ نَ بَابِيلَ دَ سُواْجُواْجِنْسَ؞ عَمَّا دُكْدَهَكَ، بَايَنْ وَنَّنْ مُتَنٜىٰ ذَاسُ سَاكٜىٰيِنْ ذَمَ عَڧَسَرْ مَصَرْ كَمَرْ يَدَّ عَكَيِ أَدَا؞ نِے يَهْوٜىٰهْ نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan bashe su a hannun waɗanda suke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa.