Jeremiah 49:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَمَرْ يَدَّ ذَاكِ يَكَنْ ٻُلُّواْ دَغَ ثِكِنْ كُرْمِ نَبَاكِنْ كُواْغِنْ يُواْدَنْ يَكُمَ كُواْرِ غَرْكٜىٰنْ تُمَكِ دَغَ ڢِيلِنْ كِيوُاْ، حَكَ ذَنْ كُواْرِ عٜىٰدُوامْ ڢَرَتْ طَيَ دَغَ ڧَسَرْتَ؞ شُوغَبَنْدَ ذَنْ ذَاٻَا، شِے ذَيْ يِمُلْكِنْتَ؞ غَمَا وَنٜىٰنٜىٰ كَمَرْنِ؟ وَ كُمَ ذَيْ عِيَيِنْ ڧَارَتَ؟ إِنَا مَكِيَايِنْ دَ ذَيْ عِيَ ڟَيَاوَا يَيِ غَابَادَنِے؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa yake kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni?