Jeremiah 49:20 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ حَكَ، كُجِ شِرِنْ دَنِے يَهْوٜىٰهْ نَيِ غَمٜىٰدَ عٜىٰدُوامْ دَ أَبِنْدَ نَكٜىٰ نُڢِ عَكَنْ مَذَوْنَنْ تٜىٰمَنْ؞ «لَلَّيْ ذَاعَ تَڢِے دَ ڧَنَانَا نَغَرْكٜىٰنْ تُمَكِ، لَلَّيْ وُرِنْ كِيوُانْسُ ذَيْ ذَمَ أَبِنْ ڟُواْرُواْ، سَبُواْدَ ذَاعَ ݣُوشِ مُتَنٜىٰ كَمَرْ تُمَكِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su.