Jeremiah 49:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِنِ عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا ، غَاشِ، ذَنْ كَٰوُاْ مُكُ أَبِنْ ڟُواْرُواْ دَغَ دُكَنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَكُو؞ ذَاعَكُواْرٜىٰكُ، كُواْوَنّٜىٰنْكُ ذَيْبِے تَاسَ حَنْيَ، بَابُوَنْدَ ذَيْ تَتَّارَ یَنْ غُدُنْ نٜىٰمَنْ ڟِيرَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ga shi, zan kawo muku razana daga waɗanda suke kewaye da ku, Za a kore ku, kowane mutum zai kama gabansa, Ba wanda zai tattara 'yan gudun hijira. Ni Ubangiji Allah Mai Runduna na faɗa.