Jeremiah 5:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ يَثٜىٰ، «عَبِے كُواْوَنٜىٰ تِيتِنْ عُرُوشَلِيمَ، أَدُدُّوبَ أَ لُورَ! عَبِنْثِكَ ڢِيلِ نَثِكِنْ غَرِ أَغَنِ، كُواْ ذَاعَ عِيَ سَامُنْ مُتُمْ طَيَ وَنْدَ يَعَيْكَتَ أَدَلْثِے، كُواْ وَنْدَ يَكٜىٰسُوانْ غَسْكِيَ، دُواْمِنْ إِنْ غَاڢَرْتَا وَبِرْنِنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ku bi titunan Urushalima ko'ina! Ku dudduba ku lura! Ku bincika kowane dandali, ku gani, Ko za ku iya samun ko mutum ɗaya Mai aikata adalci, mai son gaskiya, Sai in gafarta mata.