Jeremiah 5:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُواْمِنْ حَكَ ذَاكِ دَغَ كُرْمِ ذَيْ كَشٜىٰسُ، ݣَرْكٜىٰثِ كُمَ دَغَ هَمَادَ ذَيْ هَلَكَاسُ؞ دَامِسَ تَنَيِ وَبِرَنٜىٰنْسُ ݣُونْتُوانْ ٻَوْنَ، دُكْ وَنْدَ يَڢِتَ دَغَ ثِكِنْسُ، سَيْ عَيَيَّاغٜىٰشِ، غَمَا صَاٻُواْ صَاٻُوانْسُ سُنْيِيَوَ، رَشِنْ أَمِنْثِنْسُ بَبَّنٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Domin haka zaki daga kurmi zai kashe su, Kyarkeci kuma daga hamada zai hallaka su. Damisa tana yi wa biranensu kwanto, Duk wanda ya fita daga cikinsu sai a yayyage shi, Domin laifofinsu sun yi yawa, Karkacewarsu babba ce.