Jeremiah 50:29 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ku kira ’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«عَكِرَا مَاسُ ڢَطَ دَ بَكَ سُذُواْ سُڢَاطَوَ بَابِيلَ، دُكَنْ مَاسُ يَاڧِ دَ بَكَ سُكٜىٰوَيٜىٰ بَابِيلَ؞ كَدَ عَيَرْدَ وَنِ يَڟِيرَا؞ أَ يِ رَامُوَا عَكَنْتَ بِسَغَ أَيُّكَنْتَ، عَيِمَتَ دَيْدَيْ يَدَّ تَعَيْكَتَ، غَمَا تَايِ وَ يَهْوٜىٰهْ رٜىٰنِ، شِے وَنْدَ يَكٜىٰ مَيْ ڟَرْكِے نَ إِسْرَٰٓءِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ku kirawo 'yan baka, dukan waɗanda sukan ja baka, su faɗa wa Babila. Ku kafa sansani kewaye da ita, kada ku bar kowa ya tsira. Ku sāka mata bisa ga dukan ayyukanta, gama ta raina Ubangiji Mai Tsarki na Isra'ila.