Jeremiah 50:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«مُتَنٜىٰنَ كَمَرْ تُمَكِنْ دَ سُكَ ٻَتَ نٜىٰ، وَطَنْدَ مَكِيَايَنْسُ سُكَسَا سُنْ ٻَتَ؞ مَكِيَايَنْسُ سُكَ بَرْسُ سُيِ يَٰوُاْ عَتُدَّيْ، تُمَكِينَ سُنَ يَٰوُاْ بَرْكَتَيْ عَثِكِنْ تُدَّيْ، سُنْ مَنْتَادَ وُرِنْ هُوتُنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Mutanena sun zama kamar ɓatattun tumaki, Waɗanda makiyayansu suka bauɗar da su, Suka ɓata a cikin tsaunuka, Suna kai da kawowa daga wannan dutse zuwa wancan. Sun manta da shingensu.