Jeremiah 51:58 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ni Ubangiji Maɗaukaki, na ce, “Za a baje katangan nan na Babilon mai kauri za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta; mutane sun wahalar da kansu a banza, al’umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَتَنْ‌غَ مَيْ ڢَاطِنَّنْ نَ بَابِيلَ، ذَاعَ رُشٜىٰتَ حَرْ ڧَسَا، ڧُواْڢُواْڢِنْتَ مَاسُ ڟَيِنَّنْ، ذَاعَ ڧُواْنٜىٰ دَ وُتَا؞ ڧُواْڧَرِنْ مُتَنٜىٰنْتَ ذَيْ ذَمَ عَبَنْظَ، ڧَبِيلُنْ دُونِيَا ذَاسُ غَاجِيَرْ دَ كَنْسُ عَبَنْظَ، غَمَا وُتَا ذَاتَ ثِنْيٜىٰ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce, Za a baje garun nan na Babila mai fāɗi Za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta. Mutane sun wahalar da kansu a banza. Sauran al'umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.”