Jeremiah 6:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba; ku nemi hanyoyin dā, ku tambaya inda hanyar mai kyau take, ku yi tafiya a kanta, za ku kuwa sami hutu wa rayukanku. Amma kun ce, ‘Ba za mu bi ta ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «كُڟَيَ عِنْدَ هَنْيُواْيِ سُكَ حَطُ، كُدُوبَ، كُيِ تَمْبَيَ عَكَنْ هَنْيُواْيِنْ دَا، كُيِ تَمْبَيَ عَكَنْ حَنْيَ مَيْݣَوْ؞ كُيِ تَڢِيَ أَ حَنْيَرْ نَنْ، كُسَامِ هُوتَوَا دُواْمِنْ رَايُكَنْكُ؞ عَمَّا كُكَثٜىٰ، ‹بَذَامُيِ تَڢِيَ أَ حَنْيَرْ نَنْبَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Haka Ubangiji ya ce, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba, Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya mai kyau take, Ku bi ta, don ku hutar da rayukanku. Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’