Jeremiah 8:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتَنٜىٰنْ يَهُودَ سُنْ ثٜىٰ، «دُوانْمٜىٰ مُكٜىٰ ظَوْنٜىٰ كَوَيْ؟ مُتَتَّارُ مُتَڢِے ثِكِنْ بِرَنٜىٰ مَاسُ كَتَنْغَ، مُهَلَّكَ عَثَنْ؞ غَمَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْمُ يَڧَدَّرَمُ مُهَلَّكَ، يَكُمَ بَامُ ضُوَ مَيْ دَڢِ مُشَا، سَبُواْدَ مُنْيِ وَ يَهْوٜىٰهْ ذُنُوبِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutanen Urushalima sun ce, “Don me muke zaune kawai? Bari mu tattaru, mu tafi cikin garuruwa masu garu, Mu mutu a can, Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa, Ya ba mu ruwan dafi, Domin mun yi masa laifi.