Joel 2:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَرِ ڢِرِسْتُواْثِے مَاسُ حِدِمَرْ يَهْوٜىٰهْ أَڟَكَانِنْ ذَوْرٜىٰ دَ بَغَدٜىٰ سُيِ كُوكَا؞ بَرِ سُثٜىٰ «يَا يَهْوٜىٰهْ ، جِ تَوْسَيِنْ مُتَنٜىٰنْكَ؞ كَدَ كَسَا جَمَعَرْ غَادُوانْكَ سُكُنْيَاتَ، حَرْ أَلْعُمَّيْ سُيِ مُلْكِنْسُ؞ دُوانْمٜىٰ ذَاعَ ثٜىٰ عَثِكِنْ ڧَبِيلُ ‹إِنَا اللَّهْ نْسُ يَكٜىٰ؟› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai firistoci masu hidimar Ubangiji, Su yi kuka a tsakanin shirayi da bagade, Su ce, “Ya Ubangiji, ka ceci jama'arka, Kada ka bar gādonka ya zama abin zargi Da abin ba'a a tsakiyar al'ummai. Don kada al'ummai su ce, ‘Ina Allahnsu?’ ”