John 21:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِيسَىٰ يَسَاكٜىٰ تَمْبَيَرْسَ سَوْ نَبِيُ يَثٜىٰ «سِيمَنْ طَنْ يَحْيَى، كَنَ ڧَوْنَتَ؟» يَأَمْسَ يَثٜىٰ «عِ، عُبَنْ‌غِجِ ، أَيْ، كَا سَنْ إِنَ سُوانْكَ؞» عِيسَىٰ يَثٜىٰ مَسَ «كَيِ كِيوُانْ تُمَكِينَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya sāke faɗa masa, faɗa ta biyu, “Bitrus ɗan Yahaya, kana ƙaunata?” Ya ce masa, “I, ya Ubangiji, ka dai sani ina sonka.” Yesu ya ce masa, “Ka kiyaye tumakina.”