John 21:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بِتْرُسْ يَجُويَ يَدُوبِے بَايَ، سَيْ يَغَ أَلْمَجِرِنَّنْ دَ عِيسَىٰ يَكٜىٰ ڧَوْنَ يَنَ بِنْسُ؞ وَنَّنْ شِينٜىٰ أَلْمَجِرِنْدَ يَجِنْغِنَ عَڧِرْجِنْ عِيسَىٰ أَ لُواْكَثِنْ ثِنْ عَبِنْثِنْ بِكٍ ڧٜىٰتَرٜىٰوَ؞ شِينٜىٰ وَنْدَ يَتَمْبَيِ عِيسَىٰ يَثٜىٰ «يَا عُبَنْغِجِ ، وَنٜىٰنٜىٰ ذَيْ بَاشٜىٰكَ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Bitrus ya waiwaya ya ga almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana biye da su, wato wanda ya jingina gab da Yesu lokacin cin jibin nan da ya ce, “Ya Ubangiji, wane ne zai bāshe ka?”