John 9:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَأَمْسَ يَثٜىٰ «مُتُمِنَّنْ دَ عَكٜىٰ ثٜىٰ دَشِ عِيسَىٰ نٜىٰ يَݣُوٻَ ڧَسَا يَشَاڢَ مِنِ أَعِدَانُو، يَثٜىٰ مِنِ، ‹جٜىٰكَ كَوَنْكٜىٰ عِدُواْ أَ ضُوً سِلُوَمْ؞› نَا كُوَ جٜىٰ نَا وَنْكٜىٰ، سَيْ نَسَامِ غَنِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya amsa ya ce, “Mutumin nan da ake kira Yesu ne ya cuɗa ƙasa ya shafa mini a idanu, ya ce mini, ‘Je ka Siluwam ka wanke ido.’ Na kuwa je na wanke, sai na sami gani.”