Joshua 11:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Isra’ilawa suka kwashi ganima da dabbobi na waɗannan birane, amma suka karkashe mutanen duka da takobi, ba su bar wani mai numfashi ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِسْرَٰٓءِيلَاوَا كُمَ سُكَ ݣُوشٜىٰ وَكَنْسُ دُكَنْ أَبُبُوَ مَاسُ ݣَوْ دَ دَبُّواْبِے دَغَ وَطَنَّنْ بِرَنٜىٰ؞ عَمَّا سُكَ كَشٜىٰ كُواْوَنٜىٰ مُتُمْ دَ تَكُواْبِے، حَرْ سُكَ هَلَّكَرْ دَسُو، بَسُ ضَغٜىٰ كُواْ طَيَبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Isra'ilawa kuma suka kwashe ganima ta abubuwa masu tamani na biranen game da shanu, amma suka kashe kowane mutum da takobi, har suka hallakar da su, ba su bar kowa ba.