Joshua 11:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji kuwa ya ba Isra’ilawa nasara a kan su, suka ci su da yaƙi, suka fafare su har zuwa Sidon Babba, zuwa Misrefot Mayim, har zuwa Kwarin Mizfa a gabas, ba wanda suka bari da rai.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَهْوٜىٰهْ كُوَ يَبَادَسُو غَ حَنُّنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا؞ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا سُكَ يَاڧٜىٰسُ، سُكَ كُمَ كُواْرٜىٰسُ حَرْ ذُوَا سِدُوانْ بَبَّ دَ مِسْرٜىٰڢُواتْ مَيِمْ عَ أَرٜىٰوَ، حَرْ ذُوَا ݣُورِنْ مِظْڢَ أَغَبَسْ؞ سُكَ ثِيغَبَدَ يَاڧٜىٰنْسُ، حَرْ سُكَ كَكَّشٜىٰسُ، بَسُ ضَغٜىٰ كُواْ طَيَبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya ba da su a hannun Isra'ilawa, suka kuwa ɗibge su, suka runtume su, har zuwa Sidon Babba, da Misrefot-mayim, har zuwa gabashin kwarin Mizfa. Suka karkashe su ƙaƙaf.