Joshua 13:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمٜىٰ دَ دُكَنْ مَذَوْنَنْ يَنْكِنْ سِدُوانْ، وَطَنْدَ سُكٜىٰ ظَوْنٜىٰ عَثِكِنْ يَنْكِنْ تُدَّيْ ڟَكَانِنْ مَنْيَنْ تُدَّنْ لٜىٰبَنُوانْ دَ مِسْرٜىٰڢُواتْ مَيِمْ، نِے دَكَيْنَ ذَنْ كُواْرٜىٰسُ دُكَ دَغَ غَبَنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا؞ كَتَبَّتَا كَرَبَوَ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا يَنْكِنَّنْ يَذَمَ غَادُوانْسُ كَمَرْ يَدَّ نَعُمَرْثٜىٰكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
da dukan mazaunan ƙasar tuddai, tun daga Lebanon zuwa Misrefot-mayim har da dukan Sidoniyawa. Ni da kaina zan kore su a gaban jama'ar Isra'ila. Kai kuwa za ka raba wa Isra'ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka.