Joshua 14:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنْذُ سَيْ كَبَا نِے وَنَّنْ يَنْكِنْ تُدَّيْ وَنْدَ يَهْوٜىٰهْ يَيِ مِنِ أَلْڧَوَرِ أَ رَانَرْ دَ یَنْعُوَنَ دَنِے مُكَ بَادَ رَهُواْتُواْ؞ كَيْمَا دَكَنْكَ كَاجِ يَدَّ إِرِنْ ڧَتِّ وَطَنْدَ عَكٜىٰ كِرَنْسُ أَنَكَاوَا سُنَ ثَنْ أَ مَنْيَنْ بِرَنٜىٰ مَاسُ كَتَنْ‌غَ؞ وَتَڧِيلَ يَهْوٜىٰهْ ذَيْتَيْمَكٜىٰنِ إِنْكُواْرٜىٰسُ كَمَرْ يَدَّ يَڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Saboda haka sai ka ba ni ƙasar tuddai da Ubangiji ya ambata a ranan nan, gama a wannan rana ka ji yadda gwarzaye suke a can da manyan birane masu garu, mai yiwuwa ne Ubangiji zai kasance tare da ni, in kore su kamar yadda Ubangiji ya faɗa.”