Joshua 15:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَغَ نَنْ إِيَاكَرْ تَهَوْرَ ذُوَا ݣُورِنْ هِنُّوامْ عَكُدَنْثِنْ غَنْغَرٜىٰنْ بِرْنِنْ يٜىٰبُسْ، وَتُواْ عُرُوشَلِيمَ؞ دَغَ نَنْ إِيَاكَرْ تَهَوْرَ ذُوَا كَنْ تُدُ وَجٜىٰنْ يَمَّثِنْ ݣُورِنْ هِنُّوامْ عَبَاكِنْ ݣُورِنْ رٜىٰڢَيَاوَا عَ أَرٜىٰوَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Daga nan iyakar ta bi ta kwarin ɗan Hinnom a wajen kudancin kafaɗar Yebus, wato Urushalima. Ta kuwa bi ta dutsen da yake shimfiɗe daura da kwarin Hinnom wajen yamma, a arewacin ƙarshen kwarin Refayawa.