Joshua 19:47 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
(Amma ya zama wa mutanen kabilar Dan da wahala su mallaki ƙasar da aka ba su gādo, saboda haka sai suka nufi Leshem suka ci su da yaƙi, suka karkashe mutanen wurin, suka mallake ta, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato, Dan.)
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا ذُرِيَرْ دَنْ سُنْ شَا وَهَلَ دَ سُكَ سُواْ سُمَلَّكِ يَنْكِنْسُ، سَيْ سُكَ تَڢِے سُكَ يَاڧِ لٜىٰشٜىٰمْ؞ سُكَثِتَ دَيَاڧِ، سُكَ كَكَّشٜىٰ مُتَنٜىٰنْتَ دَ تَكُواْبِے، سُكَ مَلَّكِ ڧَسَرْ؞ سُكَ ذَوْنَ عَثِكِنْتَ، سُكَ كُمَ ثَنْجَ سُونَنْ بِرْنِنْ دَغَ لٜىٰشٜىٰمْ ذُوَا سُونَنْ كَكَنْسُ، وَتُواْ دَنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da Danawa suka rasa karkararsu, suka tafi, suka yaƙi Leshem. Da suka ci ta, sai suka hallaka mutanenta da takobi, suka mallaki ƙasar, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato Dan.