Joshua 2:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Yoshuwa ɗan Nun ya aika ’yan leƙen asiri guda biyu a ɓoye daga Shittim ya ce, “Ku je ku duba, ku ga yadda wurin yake, musamman Yeriko.” Sai suka je suka shiga gidan wata karuwa mai suna Rahab, suka sauka a can.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يُواْشُوَ طَنْ نُنْ يَعَيْكِ مُتُمْ بِيُ یَنْ لٜىٰڧٜىٰنْ أَسِيرِنْ ڧَسَا دَغَ شِتِّمْ دَ عُمَرْنِ ثٜىٰوَ «كُتَڢِے عَٻُواْيٜىٰ كُبِنْثِكَ أَسِيرِنْ ڧَسَرْ، مُسَمَّنْ بِرْنِنْ يٜىٰرِكُواْ؞» دَسُكَ تَڢِے ثِكِنْ بِرْنِنْ، سُكَ شِغَ غِدَنْ وَتَ كَارُوَ مَيْ سُونَ رَهَبْ دَ دَرٜىٰ سُكَ ݣُونَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Joshuwa ɗan Nun ya aiki mutum biyu 'yan leƙen asirin ƙasa daga Shittim a asirce, ya ce musu, “Tafi, ku leƙo asirin ƙasar, musamman Yariko.” Suka tafi, suka shiga gidan wata mace, karuwa, sunanta Rahab, a nan suka sauka.