Joshua 22:30 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da Finehas firist, da shugabannin mutanen, shugabannin iyalan Isra’ila, suka ji abin da mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse suka ce, sai suka ji daɗi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڢِنٜىٰهَسْ ڢِرِسْتِ دَ شُوغَبَنِّنْ جَمَعَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ، وَتُواْ شُوغَبَنِّ غُواْمَ نَدَنْغِنْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا، سُكَجِ مَغَنَرْ مُتَنٜىٰنْ ذُرِيَرْ رَعُبَيْنُ دَ ذُرِيَرْ غَدْ دَ رَبِنْ ذُرِيَرْ مَنَسّٜىٰ؞ دَ سُكَجِ وَنَّنْ بَيَانِ، سَيْ سُكَ غَانٜىٰ سُكَ كُمَجِ دَاطِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da Finehas, firist, da shugabannin jama'a, wato shugabannin iyalan Isra'ila, suka ji maganar da Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka faɗa, suka ji daɗi a rai.