Joshua 22:4 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yanzu da Ubangiji Allahnku ya ba ’yan’uwanku hutu kamar yadda ya yi alkawari, sai ku koma gidajenku a ƙasar da Musa bawan Ubangiji ya ba ku a Urdun.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنْذُ دَيْ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَبَا یَنْعُوَنْكُ هُوتُ، كَمَرْ يَدَّ يَيِ أَلْڧَوَرِ؞ سَبُواْدَ حَكَ، سَيْ كُكُواْمَ غِدَاجٜىٰنْكُ عَثِكِنْ ڧَسَرْكُ تَغَادُواْ وَدَّ مُوسَٰى بَاوَنْ يَهْوٜىٰهْ يَبَاكُ عَڧٜىٰتَرٜىٰنْ كُواْغِنْ يُواْدَنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu Ubangiji Allahnku ya ba 'yan'uwanku hutawa kamar yadda ya faɗa, yanzu dai sai ku koma, ku tafi gida a ƙasarku ta gādo wadda Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku a hayin Urdun.