Joshua 23:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ كُتَبَّتَا يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ بَذَيْ دِنْغَ كُواْرَرْ أَلْعُمَّنَّنْ دَغَ غَبَنْكُبَ؞ مَيْمَكُوانْ حَكَ، ذَاسُ ذَمَ مُكُ دُوڟٜىٰنْ تُنْتُٻٜىٰ دَ كُمَ تَرْكُواْ أَغَرٜىٰكُ دَ بُلَلَ مَيْ ذَاڢِ عَبَايَنْكُ دَ ڧَيُواْيِ أَعِدَنُونْكُ؞ ذَاعَثِيغَبَ حَكَ حَرْ سَيْ كُنْ ڧَارٜىٰ دَغَ وَنَّنْ ڧَسَا مَيْݣَوْ، وَدَّ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَبَاكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
to, sai ku tabbata Ubangiji Allahnku ba zai dinga korar al'umman nan daga gabanku ba, za su zama muku azargiya, da tarko, da bulala a kwiyaɓunku, da ƙayayuwa a idanunku. Da haka za ku ƙare sarai daga cikin kyakkyawar ƙasan nan da Ubangiji Allahnku ya ba ku.