Joshua 23:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عِدَنْ ڢَا كُكَ كَرْيَ وَنَّنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَرْ دَ يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْكُ يَعُمَرْثٜىٰكُ، كُكَ تَڢِے كُكَ بَوْتَاوَ أَلُّواْلِ، كُكَ كُمَ رُسُنَ مُسُ، يَهْوٜىٰهْ ذَيْ يِڢُشِے دَكُو؞ ذَاكُ كُوَ هَلَّكَ دَ سَوْرِ دَغَ ڧَسَرْ نَنْ مَيْݣَوْ وَدَّ يَبَاكُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Lokacin da kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku da ya umarce ku, kuka tafi kuka bauta wa gumaka, kuka sunkuya musu, to, Ubangiji zai yi fushi da ku, zai kuwa hallaka ku daga ƙasa mai albarka da aka ba ku.”