Joshua 24:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji Allahnmu ne da kansa ya fitar da iyayenmu daga Masar, daga ƙasar bauta, ya yi manyan abubuwan al’ajabi, a idanunmu. Ya kiyaye mu cikin dukan hanyar da muka bi, da cikin ƙasashen da muka ratsa;
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا شِے يَهْوٜىٰهْ اللَّهْ نْمُ نٜىٰ يَڢِتَرْ دَمُو دَ كَاكَنِّنْمُ دَغَ مَصَرْ دَغَ غِدَنْ بَوْتَا؞ شِينٜىٰ يَعَيْكَتَ مَنْيَنْ عَلَمُ أَعِدُوانْمُ؞ يَكِيَايٜىٰمُ عَثِكِنْ دُكَنْ حَنْيَرْ دَ مُكَبِے دَ كُمَ ثِكِنْ دُكَنْ أَلْعُمَّنْ دَ مُكَبِے تَڧَسَرْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama Ubangiji Allahnmu ne ya fisshe mu da kakanninmu daga ƙasar Masar, a gidan bauta. Shi ne wanda ya aikata manyan alamu a idonmu, ya kuma kiyaye mu a dukan hanyar da muka bi, da cikin dukan al'umman da muka ratsa.