Joshua 24:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yoshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba gama shi Allah mai tsarki ne; mai kishi kuma. Ba zai gafarta muku zunubin tawaye ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يُواْشُوَ يَثٜىٰ وَمُتَنٜىٰنْ، «عَمَّا بَذَاكُ عِيَ بَوْتَاوَ يَهْوٜىٰهْ بَ، غَمَا شِے اللَّهْ مَيْ ڟَرْكِے نٜىٰ، شِ اللَّهْ نٜىٰ مَيْ بُڧَاتَرْ ثِكَكِّيَرْ ڧَوْنَ؞ بَذَيْ غَاڢَرْتَ تَيَرْوَرْكُ دَ ذُنُبَنْكُبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Amma Joshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, gama shi Allah mai tsarki ne, mai kishi kuma, ba kuwa zai gafarta laifofinku da zunubanku ba.