Joshua 4:18 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَظَرَرْ ڢِرِسْتُواْثِے مَاسُ طَوْكٜىٰ دَ عَݣُوتِنْ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَ نَ يَهْوٜىٰهْ سُكَ ڢِتُواْ دَغَ ڟَكِيَرْ كُواْغِنْ، سَيْ ضُوً يَنَرْكٜىٰ يَڢَارَ غُدُ يَثِكَ حَرْ يَڢِتَ تَبَاكِنْ كُواْغِنْ كَمَرْ دَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka fito daga tsakiyar Urdun, suka taka sandararriyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya malalo ya tumbatsa kamar dā.