Jude 1:4 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نَڢَطِ وَنَّنْ نٜىٰ سَبُواْدَ وَطَنْسُ مُتَنٜىٰنْ دَ سُكَ شِغَ ثِكِنْكُ عَٻُواْيٜىٰ، وَطَنْدَ تُنْدَا عَكَ ڧَدَّرَسُ غَ حُكُنْثِ؞ بَاسُدَ حَلِ إِرِنْ نَ اللَّهْ ، سُنَ كُمَ مَيْدَ أَلْحٜىٰرِنْ اللَّهْ يَا ذَمَ حَنْيَرْ نٜىٰمَنْ جِنْ دَاطِے نَرَشِنْ كُنْيَا؞ سُنَيِنْ مُسُونْ عِيسَىٰ أَلْمَسِيحُ وَنْدَ شِينٜىٰ كَطَيْ شُوغَبَنْمُ دَ كُمَ عُبَنْ‌غِجِنْمُ ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gama waɗansu mutane sun saɗaɗo a cikinku, waɗanda tun zamanin dā aka ƙaddara ga hukuncin nan, marasa bin Allah ne, masu mai da alherin Allah dalilin aikata fajirci, suna kuma ƙin makaɗaicin Ubangijinmu Yesu Almasihu.