Judges 16:31 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan ’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَغَ بَايَ یَنْعُوَنْسَ دَ سَوْرَنْ دَنْ‌غِنْ عِيَلِنْسَ سُكَ غَنْ‌غَرُواْ سُكَ طَوْكِ غَاوَرْ جِكِنْسَ، سُكَ كُواْمَرْ دَشِ غِدَا؞ سُكَ بِنّٜىٰشِ عَكَبَرِنْ بَابَنْسَ مَنُواْوَ وَنْدَ يَكٜىٰ أَڟَكَانِنْ ذُواْرَ دَ عٜىٰشْتَوُالْ؞ شَمْشُونَ يَشُوغَبَنْثِ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ شٜىٰكَرَا عَشِرِنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
'Yan'uwansa da dukan danginsa, suka gangara, suka ɗauki gawarsa, suka binne a kabarin Zora da Eshtawol. Samson ya shugabanci Isra'ilawa shekara ashirin.