Judges 18:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa ’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتُمْ بِيَرْ طِنَّنْ وَطَنْدَ دَا سُكَ تَڢِے سُكَيِ لٜىٰڧٜىٰنْ أَسِيرِنْ يَنْكِنْ لَيِشْ سُكَثٜىٰ وَ أَبُواْكَنْسُ «كُواْ كُنْ سَنِ ثٜىٰوَ عَثِكِنْ طَيَ دَغَ غِدَاجٜىٰنَّنْ، أَݣَويْ غُنْكِ نَ إِتَاثٜىٰنْ دَ عَكَ شَاڢَ دَ أَظُرْڢَا؟ أَݣَويْ كُمَ وَطَنْسُ غُمَكَ دَ كُمَ عٜىٰڢُوادْ نَنٜىٰمَنْ سَنِنْ نُڢِنْ اللَّهْ ؞ مٜىٰ يَا كَمَاتَ مُيِ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutum biyar ɗin nan da suka tafi leƙen asirin ƙasar Layish, suka ce wa abokan tafiyarsu, “Ko kun san akwai gunkin itace cikin gidajen nan? Akwai kuma gunki na zubi, da kan gida, da falmaran dominsu. Me ya kamata mu yi musu?”