Judges 18:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ مُتَنٜىٰنْ دَنْ سُكَ ذَاٻِ مُتُمْ بِيَرْ مَاسُ ڧَرْڢِنْ ذُوثِيَا دَغَ دَنْغُواْغِنْ ذُرِيَرْسُ؞ عَكَ كُوَ عَيْكٜىٰسُ دَغَ غَرُضُوً ذُواْرَ دَ عٜىٰشْتَوُالْ سُتَڢِے سُلٜىٰڧِ أَسِيرِنْ ڧَسَرْ؞ سَعَدَّ سُكَ إِسُواْ يَنْكِنْ تُدَّيْ نَ إِڢْرَيِمْ، سَيْ سُكَ سَوْكَ أَغِدَنْ مِيكَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Danawa suka zaɓi mutum biyar jarumai daga kabilarsu, suka aike su daga Zora da Eshtawol, su tafi leƙen asirin ƙasar, su bincike ta. Suka kuwa tafi zuwa ƙasar tudu ta Ifraimu, suka sauka a gidan Mika.