Judges 2:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Cikin fushinsa a kan Isra’ila Ubangiji ya ba da su ga hannun waɗanda suka kawo musu hari suka washe su. Ya sayar da su ga abokan gābansu da suke kewaye da su, waɗanda ba za su iya yin tsayayya da su ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُواْمِنْ حَكَنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ يَيِ ڢُشِے مَيْ ذَاڢِ دَ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، يَبَاشٜىٰسُ أَ حَنُّنْ مَاسُ ڨُوثٜىٰ كَايَنْسُ دَ عَبِنْثِنْسُ؞ يَهْوٜىٰهْ يَسَا أَبُواْكَنْ غَابَنْدَ سُكٜىٰ كٜىٰوَيٜىٰ دَسُو سُكَشَا ڧَرْڢِنْسُ؞ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ كُوَ بَسُ عِيَ كَارٜىٰ كَنْسُ دَغَ أَبُواْكَنْ غَابَنْسُ بَ كُمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa, ya bashe su ga waɗanda za su washe su. Ya sa magabtansu da suke kewaye da su suka sha ƙarfinsu, har ya zama Isra'ilawa ba su iya kāre kansu daga maƙiyansu ba.