Judges 21:22 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da iyayensu maza ko ’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da ’ya’yan matanku gare su ba.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
حَڧِيڧَ إِيَايٜىٰنْسُ دَ یَنْعُوَنْسُ ذَاسُذُواْ سُيِ ڧَارَرْكُ أَوُرِنْمُ؞ سَعَدَّ سُكَذُواْ مُو ذَامُثٜىٰ مُسُ، ‹مُنَ ضُواْڧُوانْكُ، كُيِ مُسُ كِرْكِ سَبُواْدَمُو؞ غَمَا بَمُسَامُواْ وَدُكَنْسُ مَتَ أَ لُواْكَثِنْ يَاڧِبَ؞ كُو كُمَ بَكُ جَٰوُاْ وَكَنْكُ وَنِ لَيْڢِے تَوُرِنْ كَرْيَ ضَنْڟُوَابَ، تُنْدَ بَ دَ يَرْدَرْكُ سُكَ عَوْرِ یَیَنْكُ مَتَبَ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da iyayensu ko 'yan'uwansu sun kawo ƙara gare mu, za mu ce musu, ‘Ku bar mana su, muna roƙonku, domin ba daga wurin yaƙi muka kamo su domin su zama matanmu ba. Amma tun da ba ku ba mu su ba, ba ku da laifin ta da alkawari.’ ”