Judges 21:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَا مَا أَ مِظْڢَ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا سُكَ طَوْكِ ضَنْڟُوَا ثٜىٰوَ «دُكْ وَنْدَ بَيْ تَڢِے مِظْڢَ بَ، ذَاعَ كَشٜىٰشِ؞» دَ سُكَ تَارُ أَ بٜىٰتٜىٰلْ، سُكَثٜىٰ «أَݣَويْ وَتَ ذُرِيَرْ إِسْرَٰٓءِيلَ وَدَّ بَتَكَسَنْثٜىٰ عَتَارُوانْ جَمَعَرْمُ دَ مُكَيِ أَغَبَنْ يَهْوٜىٰهْ أَ مِظْڢَ بَ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suka kuma ce, “Daga cikin kabilar Isra'ila, wace ce ba ta halarci wannan taro na gaban Ubangiji ba?” Gama sun riga sun yi ƙaƙƙarfan alkawari cewa, “Duk wanda bai hauro zuwa wurin Ubangiji a Mizfa ba, za a kashe shi.”