Judges 4:22 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
بَرَكْ كُوَ يَنَ ڢَامَرْ بِنْ سِسٜىٰرَ؞ دَ يَيٜىٰلْ مَاتَرْ هٜىٰبٜىٰرْ تَغَنْ شِ، تَاڢِتَ تَاسَامٜىٰشِ تَثٜىٰمَسَ «كَذُواْ نَنْ! ذَنْ نُونَ مَكَ عِنْدَ مُتُمِنَّنْ دَ كَكٜىٰ نٜىٰمَ يَكٜىٰ؞» سَيْ يَبِتَ ذُوَا ثِكِنْ تٜىٰنْتِنْ، يَتَرَرْ دَ جِكِنْ سِسٜىٰرَ ݣُونْثٜىٰ عَڧَسَا غَاوَا، تَرٜىٰدَ ڧُوسَرْ كَڢَ تٜىٰنْتِ عَثِكِنْ كَنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Barak kuwa yana bin sawun Sisera. Da Yayel ta gan shi, sai ta fita, ta tarye shi, ta ce masa, “Ka zo, zan nuna maka inda mutumin da kake nema yake.” Ya shiga alfarwarta, sai ga Sisera nan kwance matacce da turke a gindin kunnensa.