Judges 8:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ جِدْعَوْنَ يَتَڢِے وُرِنْ مُتَنٜىٰنْ سُكُّواتْ يَثٜىٰ مُسُ «تُواْ، غَ ظٜىٰبَ دَ ظَلْمُنَّ وَطَنْدَ كُكَيِ مِنِ بَعَ سَبُواْدَسُو، كُنَ ثٜىٰوَ ‹يَيَ ذَامُ بَ سُواْجُواْجِنْكَ مَاسُ غَاجِيَ عَبِنْثِ؟ بَكَارِغَا كَا كَامَ ظٜىٰبَ دَ ظَلْمُنَّ بَ؞› تُواْ؞ غَا سُو نَنْ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan ya zo wurin mutanen Sukkot ya ce musu, “To, ga Zeba da Zalmunna waɗanda kuka yi mini ba'a saboda su, kuna cewa, ‘Ba ka riga ka kama Zeba da Zalmunna ba, ta yaya za mu ba sojojinka da suka gaji abinci?’ To, ga su!”