Judges 9:2 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ku tambayi ’yan ƙasar Shekem, ‘Wanne ya fi muku, a sa dukan ’ya’yan Yerub-Ba’al saba’in maza su yi mulkinku, ko dai mutum guda kawai yă yi mulkinku?’ Ku tuna, ni jininku ne.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«إِنَ ضُواْڧُوانْكُ، كُيِ مَغَنَ دَ شُوغَبَنِّنْ شٜىٰكٜىٰمْ، كُثٜىٰ مُسُ، ‹مٜىٰ يَڢِ مُكُ ݣَوْ، عَثٜىٰ دُكَنْ یَیَنْ جِدْعَوْنَ غُدَا سَبَعِنْ طِنَّنْ سُيِ مُلْكِنْكُ، كُواْ كُوَ عَثٜىٰ مُتُمْ طَيَ يَيِ مُلْكِنْكُ؟› عَمَّا كُتُنَ ڢَا نِے نَامَنْكُ دَ جِنِنْكُ نٜىٰ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ina roƙonku, ku yi magana da shugabannin Shekem, ku ce, ‘Me ya fi muku kyau, 'ya'yan Yerubba'al, maza saba'in su yi mulkinku, ko kuwa mutum ɗaya ya yi mulkinku?’ Amma ku tuna fa ni jininku ne.”