Judges 9:28 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Ga’al ɗan Ebed ya ce, “Wane ne Abimelek, kuma wane ne Shekem, da za mu bauta masa? Shi ba ɗan Yerub-Ba’al ba ne, kuma ba Zebul ne mataimakinsa ba? Ku bauta wa mutanen Hamor, mahaifin Shekem! Me ya sa za mu bauta wa Abimelek?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَعَلْ طَنْ عٜىٰبٜىٰدْ يَثٜىٰ «وَنٜىٰنٜىٰ أَبِمٜىٰلٜىٰكْ، حَرْ دَ مُو مُتَنٜىٰنْ شٜىٰكٜىٰمْ ذَامُ بَوْتَا مَسَ؟ بَشِے طَنْ يٜىٰرُبَّعَلْ بَنٜىٰ؟ بَكُمَ ظٜىٰبُلْ مَعَيْكَثِنْسَبَنٜىٰ؟ دُوانْمٜىٰ ذَامُ بَوْتَا مَسَ؟ كُيِ أَمِنْثِ غَ كَكَنْكُ هَمُوارْ تُوشٜىٰنْ ڧَبِيلَرْكُ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ga'al, ɗan Ebed, ya ce, “Wane ne Abimelek har mu mutanen Shekem za mu bauta masa? Ashe, ba Yerubba'al ne mahaifinsa ba, Zebul kuma shugaban yaƙinsa? Don me za mu bauta masa? Ku yi aminci ga kakanku Hamor, tushen kabilarku!