Lamentations 1:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna. ’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَبُواْدَ وَطَنَّنْ أَبُبُوَ، إِنَ تَكُوكَا، هَوَيٜىٰ سُنَ ظُبُواْوَ دَغَ عِدَنُونَ؞ غَمَا مَيْ تَعَظَنْتَرْ دَنِے يَيِ نٜىٰسَ، وَنْدَ ذَيْ ڧَرْڢَڢَ رَيْنَ يَيِ نٜىٰسَ دَنِے؞ یَیَنَ سُنَ ذَمَنْ كَطَيْثِ، غَمَا أَبُواْكِنْ غَابَا يَيِ نَصَرَا عَكَنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ina kuka saboda waɗannan abubuwa, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf daga idanuna. Gama mai ta'azantar da ni, Wanda zai sa in murmure yana nesa da ni. 'Ya'yana sun lalace, Gama maƙiyi ya yi nasara!”