Lamentations 2:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكَنْ وَطَنْدَ سُكٜىٰ وُثٜىٰوَ سُنَ تَڢَ حَنُّنْ رٜىٰنِ سُنَ كَطَكَيْ؞ سُنَيِ وَذُوثِيَاتَ عُرُوشَلِيمَ ڟَكِ ثٜىٰوَ «أَشٜىٰ، بِرْنِ مَڢِے ݣَنْ غَنِ أَدَا كٜىٰنَنْ، أَبِنْ ڢَضٍ ثِكِ غَ دُكَنْ دُونِيَا؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini. Suna yi wa Urushalima tsāki, Suna kaɗa mata kai, suna cewa, “Ai, Urushalima ke nan, Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali, Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?”