Lamentations 2:20 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci ’ya’yansu, ’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا يَهْوٜىٰهْ ، دُوبَ، كَغَنِ! حَكَ كَسَابَايِ دَ مُتَنٜىٰ؟ يَيِ ݣَوْ إِيَايٜىٰ مَاتَا سُثِنْيٜىٰ یَیَنْسُ؟ يَيِ ݣَوْ عَكَشٜىٰ ڢِرِسْتِ دَ أَنَّبِے عَثِكِنْ وُرِے مَيْ ڟَرْكِے نَ عُبَنْغِجِ ؟
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Ubangiji, ka duba, ka gani! Wane ne ka yi wa haka? Mata za su cinye 'ya'yansu da suke reno? Ko kuwa za a kashe firist da annabi A cikin Haikalin Ubangiji?