Leviticus 10:6 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar ’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُوسَٰى يَثٜىٰ وَ هَٰرُونَ دَ یَیَنْسَ عٜىٰلٜىٰيَظَرْ دَ عِتَمَرْ «كَدَ كُبَرْ غَاشِنْ كَنْكُ بَرْكَتَيْ وَيْ كُنَ مَكُواْكِ، كُواْ كُيَيَّغٜىٰ رِيغُنَنْكُ نَڢِرِسْتِ؞ إِنْ كُنْيِ حَكَ، ذَاكُ مُتُ كُكُمَ جَٰوُاْ ڢُشِنْ اللَّهْ عَكَنْ دُكَنْ جَمَعَرْ؞ عَمَّا كُبَرْ یَنْعُوَنْكُ، وَتُواْ دُكَنْ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، سُيِ كُوكَنْ مُتُوَرْ دَ وُتَرْ يَهْوٜىٰهْ تَجَٰوُاْ مُكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Musa kuma ya ce wa Haruna, da 'ya'yansa maza, wato, Ele'azara da Itamar, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku kyakketa rigunanku don kada ku mutu, don kada Ubangiji ya yi fushi da taron jama'a duka, amma 'yan'uwanku, wato, dukan Isra'ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya ƙone.