Leviticus 16:15 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَيْ يَيَنْكَ بُنْسُرُ نَهَدَايَ تَوَنْكٜىٰ ذُنُوبِ دُواْمِنْ جَمَعَرْ، يَكَٰوُاْ جِنِنْ بَايَنْ لَبُلٜىٰنْ؞ ذَيْ يِدَشِ كَمَرْ يَدَّ يَيِ دَ جِنِنْ طَنْ بِجِمِنْ، وَتُواْ ذَيْ يَيَّڢَا شِ عَبِسَ مُرْڢِنْ عَݣُوتِنْ دَ كُمَ أَغَبَنْ مُرْڢِنْ عَݣُوتِنْ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai kuma ya yanka bunsuru na yin hadaya don zunubin jama'ar ya shigar da jinin bayan labulen. Zai sa jinin kamar yadda ya yi da jinin bijimin, ya yayyafa shi a kan murfin, da gaban murfin.