Leviticus 26:36 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“ ‘Ga waɗanda za su ragu kuwa, zan cika zukatansu da tsoro a ƙasashen abokan gābansu har motsin ganyen da iska ta hura zai sa su ruga da gudu. Za su yi gudu kamar suna gudu daga takobi ne, za su kuma fāɗi, ko da yake babu wanda yake korinsu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«عَمَّا كُو دَكُكَ رَغُ عَڧَسَاشٜىٰنْ أَبُواْكَنْ غَابَنْكُ، ذَنْسَا ظُكَاتَنْكُ سُثِكَ دَ ڟُواْرُواْ حَرْ مُواْڟِنْ غَنْيٜىٰ كَوَيْ مَا ذَيْ رَظَنَرْ دَكُو، كُشٜىٰڧَ دَ غُدُ كَمَرْ وَطَنْدَ عَكٜىٰ بِنْسُ دَ تَكُواْبِے؞ ذَاكُ كُوَ ڢَڢَّاطِ عَڧَسَا كُواْدَيَكٜىٰ بَا مَيْ كُواْرَرْكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Amma ga waɗanda suka ragu, zan sa fargaba a zuciyarsu sa'ad da suke a ƙasar maƙiyansu. Ko motsin ganye kawai ma zai razanar da su su sheƙa a guje kamar waɗanda ake fafara da takobi, ga shi kuwa, ba mai korarsu, za su kuwa fāɗi.