Luke 11:42 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«كَيْتُوانْكُ، ڢَرِسِيَاوَا! كُنَبَا اللَّهْ زَكَّرْ كَايَنْ يَجِ نَغَنْيٜىٰ دَ كُمَ سَوْرَنْ غَنْيٜىٰنْ مِيَ دُكَ؞ عَمَّا كُنْڧِ كُلَ دَ عَيْكَتَ غَسْكِيَ دَ ڧَوْنَرْ اللَّهْ ؞ وَطَنَّنْ نٜىٰ يَا كَمَاتَ كُيِ، بَاتَرٜىٰدَ كُنْ ڨَلٜىٰ سَوْرَنْبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Kaitonku, Farisiyawa! Ga shi, kuna fitar da zakkar na'ana'a da karkashi, da kuma kowane ganyen miya. Amma kun ƙi kula da aikata gaskiya da ƙaunar Allah. Waɗannan ne ya kamata ku yi, ba tare da yar da waɗancan ba.