Luke 12:37 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَيْ ذَمَ أَبِنْ ڢَضٍ ثِكِ غَ بَايِنَّنْ إِنْ حَرْ مَيْغِدَنْ يَدَاوُاْ يَسَامٜىٰسُ بَسُيِ بَرْثِبَ؞ حَڧِيڧَ إِنَ غَيَ مُكُ، ذَيْثِرٜىٰ بَبَّرْ رِغَرْدَ يَسَا، يَثٜىٰ مُسُ سُظَظْذَوْنَ، سُثِ عَبِنْثِ، سَعَنً يَبِے كَنْ كُواْوَنٜىٰ طَيَنْسُ يَكَٰوُاْ مَسَ عَبِنْثِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Albarka tā tabbata ga bayin nan waɗanda ubangijinsu da zuwansa zai same su a faɗake. Hakika, ina gaya muku, zai yi ɗamara, ya ce su zauna cin abinci, sa'an nan ya bi ta kan kowannensu yana yi masa hidima.