Luke 18:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«سَيْ بَڢَرِسِيٜىٰنْ يَتَاشِ يَڟَيَ، يَڢَارَ أَدُّعَ يَنَ ثٜىٰوَ ‹ اللَّهْ ، نَغُواْدٜىٰ مَكَ سَبُواْدَ نِے بَكَمَرْ سَوْرَنْ مُتَنٜىٰ بَنٜىٰ، مَاسُ سَاتَا، مَاسُ ثُوتَا، مَاسُ ظِنَ؞ نِے بَكَمَرْ مَيْ كَرْٻَرْ هَرَاجِنَّنْ بَنٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Bafarisiyen ya miƙe, ya yi addu'a ga kansa ya ce, ‘Ya Allah, na gode maka, da yake ni ba kamar sauran mutane nake ba, mazambata, marasa adalci, mazinata, ko ma kamar mai karɓar harajin nan.