Luke 18:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عِيسَىٰ يَثٜىٰ «إِنَغَيَ مُكُ، مَيْ كَرْٻَرْ هَرَاجِنَّنْ يَكُواْمَ غِدَنْسَ دَ سَامُنْ ذَمَ مَرَرْ لَيْڢِے أَغَبَنْ اللَّهْ ، بَكَمَرْ بَڢَرِسِيٜىٰنْ بَ؞ غَمَا دُكْ وَنْدَ يَطَوْكَكَ كَنْسَ، ذَاعَ ڧَسْڧَنْتَرْ دَشِ؞ عَمَّا دُكْ وَنْدَ يَڧَسْڧَنْتَرْ دَكَنْسَ، ذَاعَ طَوْكَكَاشِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ina dai gaya muku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar ɗayan ba. Don duk mai ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Mai ƙasƙantar da kansa kuwa, ɗaukaka shi za a yi.”